Franklin Graham mutum ne da ke bayyana tsananin kiyayyarsa ga addinin muslunci da ma musulmi, inda a cikin shekara ta 2015 ya shelanta wani kamfe na kyamar msuulmi, tare da yin kira da a rufe dukkanin masallatai da cibiyoyi gami da makarantun msuulmia a kasar Amurka, saboda a cewarsa musulmi su ne 'yan ta'adda, kuma addininsu shi ne yake kira zuwa ga ta'addanci.
Haka nan kuma ya taka gagarumar rawa wajen yada kyamar musulmi a tsakanin al'ummar Amurka, musamman ma wadanda suke halartar majami'arsa ko kuma suke sauraren bayanansa.
A ranar 20 ga wannan wata ne na Janairu za a rantsar da Donald Trump a matsayin shugaban kasar Amurka, yayin da wasu 'yan majalisa 10 na jam'iyyar Democrat suka haramta wa kansu halartar taron.