Ya ce harin da aka kai ma musulmi yau da sassafe ba shi ne irinsa na farko ba, hakan na faruwa sau da dama a sassa daban-daban na kasar, inda ko mako guda ba ayi ba da cinna wuta akan wani dogon bene da musulmi ne mafi yawan mutanen da suke a cikinsa, a yau kuma an kai musu hari har a wurin ibada a cikin birnin an London.
Ya kara da cewa wadannan abubuwa suna faruwa ne sakamakon karuwar kyamar musulmia tsakanin wasu 'yan kasar ta Birtaniya, alhali musulmin da suke a kasar su ma 'yan kasa ne da suke da dukaknin hakkoki kamar kowane dan kasa, kuma a bisa doka dole ne a kare ma musulmi na hakkokin, tare da basu kariya da kuma tsaron lafiyarsu da kaddarorinsu da mutuncinsu.