Ya ce suna kiran gwamnatin Birtaniya da ta dauki dukkanin matakan da ska dace domin baiwa musulmi kariya, domin kaucewa sake faruwar irin wannan aiki na keta alfrmar addini da 'yan adamtaka, da nuna bangaranci ga wani jinsi na al'ummar kasar ta Birtaniya saboda akidarsu ta addini.
Daga karshe kuma ya kirayi musulmin Birtaniya da su ci gaba da zaman lafiya da sauran jama'a tare da kyautatawa kamar yadda musulunci ya yi umarni, haka nan kuma kada su bari ayyukan wawaye su tunzura su domin aikata abin dace da su ba.