Mar Narsai Benjamin, daya daga cikin manyan malaman addinin kirista a Iran ya bayyana marigayi Imam Khomeini a matsayin jagora na kowa da kowa, inda ba ya nuna bambanci a tsakanin al'ummar da yake jagoranta wajen yin adalci da kyautatawa a gare su, sannan kuma kasantuwarsa mutum ne wanda yake da tsananin tsoron Allah da gudun duniya, tausayi da hakuri, hakan ne yasa dukkanin al'umma suke sonsa da kaunarsa ba tare da la'akari da bambanci addini ko fahimta ba.