IQNA

Jagora Ya Amince Da Sabon Wa'adin Hasan Rouhani

21:37 - August 03, 2017
Lambar Labari: 3481762
Bangaren siyasa, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewar Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta taba kuma ba za ta taba mika kai ga mulkin kama-karya na ma'abota girman kai, yana mai cewa a halin yanzu Iran tana tsaya da kafafunta kyam sama da shekarun baya.
Kamfanin dillancin labaran IQNA ya bayar da rahoton cewa, jagoran ya bayyana hakan ne a jawabin da ya yi da safiyar yau wajen bikin tabbatar da shugaba Hasan Ruhani a matsayin shugaban kasar Iran karo na 12, inda ya ce makiya sun ci gaba da matsin lamba da kulla makirce-makirce wa Iran, don haka wajibi ne al'ummar Iran da jami'an kasar su zamanto a farke. Jagoran ya ci gaba da cewa jami'an kasar Iran sun san yadda za su tinkari wadannan makirce-makirce ba tare da tsoho ba.

Jagoran ya ci gaba da cewa: Wajibi ne jami'an gwamnati su yi la'akari da abubuwa uku, na farko yanayin tattalin arziki da yanayin rayuwar mutane, sannan su yi kokari wajen kyautata alakarsu da sauran kasashen duniya, na uku kuma su tsaya kyam wajen tinkarar girman kan ma'abota girman kan duniya.

A safiyar yau ne dai ne aka gudanar da bikin tabbatar da shugaba Ruhanin a karo na biyu na shugabancinsa. A bisa kundin tsarin mulkin Iran duk shugaban kasa da aka zaba yana bukatar amincewar Jagoran juyin juya halin Musulunci kafin yayi rantsuwar kama aiki a gaban majalisar dokokin kasar.

Shi ma anasa bangaren shugaban kasar Iran Dakta Hasan Ruhani ya bayyana cewar ko da wasa Iran ba za ta taba mika kai da kuma yarda da kokarin da makiya suke yi na mai she ta saniyar ware a tsakankanin kasashen duniya ba.

Shugaba Ruhani ya bayyana hakan ne a jawabin da yayi a wajen bikintabbatar da zabensa da aka yi a matsayin shugaban kasar Iran karo na 12 da aka gudanar a Husainiyar Imam Khumaini (r.a) karkashin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci lalle abin alfahari ne a ga al'ummar Iran da suka sami kansu karkashin inuwar tsarin Jamhuriyar Musulunci.

Yayin da yake magana kan zaben shugaban kasar da aka gudanar a kasar Iran a baya inda aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a wa'adin mulki na biyu, shugaba Ruhani ya ce hakan yana nuni da tsarin demokaradiyya na addini da ke iko a kasar Iran inda jama'a suke da bakin fadi cikin gudanar da kasa, yana mai alkawarin kare hakkokin al'umma da kasar Iran daga duk wani kokarin wuce gona da iri na makiya.

A ranar Asabar mai zuwa ce ake sa ran shugaba Ruhanin zai yi rantsuwar kama aiki a gaban 'yan majalisar shawarar Musulunci ta kasar Iran da ake sa ran shugabanni da manyan jami'an kasashe da dama na duniya za su halarta.

3626377


captcha