Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, shugaban sashin kula da lafiya na Karbala Sabah Al-Mousavi ya sanar da cewa, shirin kiwon lafiya na musamman na ranar Arba’in ya hada da raba motocin daukar marasa lafiya 100 a kusa da cibiyoyin bada agajin gaggawa a tsohon yankin na Karbala da kuma wajensa.
Ya kara da cewa: Tawagar likitoci 43 kuma suna jibge tare da gatura guda uku a tazarar kasa da kilomita 20 zuwa tsakiyar Karbala domin gudanar da ayyukan kiwon lafiya ga masu ziyara.
Al-Muusavi ya ce: An kafa asibitin filin Al-Zahra (A.S) a kusa da Amoud (880), a kan (Karbala-Najaf), sannan kuma, asibitoci takwas na gwamnati baya ga asibitoci masu zaman kansu a shirye suke don ba da hidima ga masu ziyara.
Wannan jami'in kula da lafiya na Karbala ya bayyana cewa: Tawagar ma'aikatan lafiya takwas da ke da alaka da Al-Hashd al-Sha'abi, da kuma tawagogin da ke da alaka da Haramin Hosseini da Abbasi, suna jibge a cikin gatari na tsohon yankin na Karbala.
Al-Mousavi ya kara da cewa: Tawagar kiwon lafiya 55 ne ke da alhakin sanya ido kan ruwan sha da abincin da ake baiwa masu ziyara, haka kuma, tawagogin gaggawa 60 na cikin shirin tunkarar matsalolin gaggawa da ka iya faruwa a yayin taron na Arbaeen.
Wannan jami'in ma'aikatar lafiya ta Karbala ya jaddada cewa: Haka nan kuma za a bude dakunan gaggawa a cibiyoyin kiwon lafiya, wadanda za a samar musu da dukkanin magunguna, na'urori da na'urorin kiwon lafiya na gaggawa.