Yan bindiga dake garkuwa da mutane domin karbar diyya a Najeriya, sun kai hari a kauyen Zugu dake Jihar Zamfara inda suka kwahse mutane a Masallachin Juma’ar garin wadanda suka je domin sauke farali.
Rahotanni sun ce Yan bindigar sun isa garin ne da misalin karfe 1 na rana a kasa, inda suka fara tattara mutane a Kasuwa, kafin daga bisani suka wuce Masallachin Juma’a suka kwashe masu jiran liman domin sauke farali.
Wani shaidar gani da ido a garin ya tabbatar mana aukuwar lamarin, yayin da yace jami’an tsaro cikin motoci guda 2 suna isa Zugun inda suka dauki wasu mutane 3 dan taimaka musu bin sawun barayin.
Jihar Zamfara na ci gaba da fuskantar matsalar tsaro sakamakon yadda Yan bindiga suka mamaye ta suna kai hari akan mutanen garuruwa daban daban.